1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar dokokin Zimbabwe ta fara sabon zama

July 24, 2007
https://p.dw.com/p/BuFZ

Shugaban Zimbabwe dake shan suka Robert Mugabe a yau talata ya bude sabon zama na majalisar dokokin kasar wadda ake sa rai zata amince da tsauraran shirye shiryen gwamnati na mayar da kamfanonin ketare dake kasar mallakin gwamnati gabanin babban zabe da za´a gudanar a badi. Mugabe mai shekaru 83 ya na neman a sake zaben sa a zaben na badi duk da zargin da ake masa cewa ya jefa kasar ta Zimbabwe cikin matsalolin tabarbarewar tattalin arziki sakamakon manufofin sa da ake kace nace a kai. Zimbabwe ta kasa magance matsalar hauhawar farashin kaya a cikin watannin mayu da yuni wanda ya ninka har sau 300 a cikin mako guda.