Majalisar Dokokin Jamus ta amince da aikewa da sojojin kasar zuwa Libanon
September 20, 2006Talla
A yau laraba majalisar dokokin Jamus Bundestag ta kada kuri´ar amincewa da tura dakarun kasar wadanda zasu yi aiki karkashin sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD a Lebanon. ´Yan majalisa 442 suka jefa kuri´ar amincewa da girke da dakarun kasar a Libanon, 152 suka nuna adawa da wannan mataki yayin da wakilai 5 suka yi rowar kuri´unsu. Gabanin a kada kuri´ar jam´iyun adawa guda biyu da suka hada da FDP da masu ra´ayin canji sun nuna shakku suna masu cewa ana iya samun artabu tsakanin dakaraun na Jamus da na Isra´ila. Ana ganin haka a matsayin wata matsala musamman saboda tarihin Jamus na ´yan NAZI. Jamus dai ta yi tayin ba da gudunmawar sojoji dubu 2 da 400 da zasu rika yin sintiri a gabar tekun Lebanon don hana yin sumogar makmai ga ´yan Hisbollah.