1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Ɗinkin Duniya na neman AU ta ci gaba da girke dakarunta a yankin Darfur.

July 2, 2006
https://p.dw.com/p/Burm

Babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Kofi Annan, ya ce yana ƙoƙarin ganin cewa, an tsawaita wa’adin girke dakarun kare zaman lafiya na Ƙungiyar Tarayyar Afirka, wato AU, a yankin Darfur har zuwa ƙarshen wannan shekarar, yayin da a wani ɓangaren kuma, ake ta hidmiomin cim ma yarjejeniya kan maye gurbinsu da dakarun Majalisar Ɗinkin Duniya. Da yake yi wa taron maneman labarai jawabi a taron ƙoli na Ƙungiyar AUn da ake yi a birnin Banjul na ƙasar Gambiya, Kofi Annan, ya ce ya bukaci shugabannin ƙasashen ƙungiyar da su nuna sassauci ga shirinsu na janye dakarun a ƙarshen watan Satumba, saboda rashin kuɗin da suke huskanta.

Ana dai kyautata zaton cewa, kafin rufe taron yau, shugabannin za su yanke shawara kan matakan da za a ɗauka nan gaba game da yankin na Darfur, inda yaƙin basasa da aka shafe shekaru 3 ana yi, ya janyo asarar rayukan mutane fiye da dubu ɗari 3.