1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An hana duk wani taron adawa a Kwango

Yusuf BalaOctober 20, 2015

An dai katse hanyoyin sadarwa a birnin Brazzaville kafin fara gangamin da zai yi adawa da shirin kuri'ar raba gardama ranar Lahadi.

https://p.dw.com/p/1Gqz1
Kongo Präsident Denis Sassou-Nguesso
Shugaba Denis Sassou NguessoHoto: AP

Mahukunta a Jamhuriyar Dimokradiyar Kwango a ranar Talatan nan sun haramta duk wani nau'i na zanga-zanga bayan da bangaren adawa suka shirya gangami na nuna kin amincewa da ci gaba da makalewa a kan mulki da shugaban kasar ke yi bayan kuwa ya zauna a wannan kujera gwamman shekaru.

An dai katse hanyoyin sadarwa a birnin Brazzaville kafin fara gangamin da zai yi adawa da shirin kuri'ar raba gardama ranar Lahadi, da za ta ba wa shugaba Denis Sassou Nguesso damar yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar yadda zai samu damar yin tazarce a wani sabon wa'adi na mulkin wannan kasa. Tun daga 1997 ne shugaban ke kan mulki bayan wani yakin basasa da kasar ta shiga. Tun dai a baya ma a shekarun 1979 zuwa 1992 shugaba Nguesso ya mulki wannan kasa ta Kwango.

Sa'oi dai kafin bayyanar wannan sanarwar haramta gamgamin a ranar Talatan nan, 'yan sanda ta hanyar amfani da hayaki mai sa hawaye sun tarwatsa matasa masu zanga-zanga da ke kona tayoyi a tituna a kudancin lardin Bacongo da Makelekele kamar yadda wani ganau ya shedar.