Mahmud Abbas zai kiri zaɓen raba gardama
June 6, 2006Shugaban hukumar Palestinawa Mahamud Abbas, ya jagoranci wani mahimmin taro, da komitin zartaswa, na ƙungiyar PLO, a game da batun ƙuri´ar raba gardama, da ya ambaci shirya wa a ƙasar , da zumar jin ra´ayin jama´a, a kan hanyoyin warware rikici tsakanin Palestinu da Isra´ila.
Manyan jami´an Palestninu, na ɓangarori daban daban, da ke kulle a gidajen kurkukun Isreala, su ka gabata da wassu mattakai, wanda a tunanin su, za su samar da zaman lahia, tsakakin ƙasashenn 2, to saidai gwamnatin Hamas, mai tsatsauran ra´ayi, ta yi watsi da wannan shawarwari.
A taƙaici wannan kundi, ya shawarci dakatar da kai hare hare, ga Isra´ila, da kuma amincewa da iyakokin shekara ta 1967, da su ka raba ƙasashen 2.
Hakan na nufi, a fakaice amincewa, da ƙasar Isra´ila, batun da gwamnatin Hamas ke adawa da shi.
A sakamakon taron na yau, ƙungiyar OLP ta baiwa Mahamud Abbas goyan baya,wajen shirya wannan zaɓe.
Abbas ya yanke shawara shirya ƙuri´ar, jin ra´ayin jama´ar, a sakamakon taƙƙadamar da aka fuskanta, a tantanawa tsakakin Hamas da Fatah, da sauran ɓangarorin ƙasar, na tabatar da kwanciyar hankali, da kuma warware matsalolin takunkumin da ƙasashen Turai da Amurika su ka sakawa Paletinu.