Manowa na cikin fargaba a Zamfara
May 27, 2018Talla
Lamarin ya faru ne a lokacin da wasu mahara suka farwa manoma da suka je shuka a gonakinsu, suka kashe su nan take. Bayan nan al'ummar gari sun je daukar gawarwakin wadanda aka kashen, 'yan bindigar suka sake dawowa suka bude musu wuta.
Sai dai kokarin jin ta bakin jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar ta Zamfara DSP Shehu Muhammad ta wayar tarho ya ci tura. Yanzu haka dai manoman wannan jiha na cikin fargaba ganin damina ta kama amma zuwa gona na neman gagararsu.