1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macin ƙin jinin gwamnatin sojin Myanmar na kara yin tsamari

September 24, 2007
https://p.dw.com/p/BuAQ

Gwamnatin tarayyar Jamus ta yi maraba da zanga-zangar lumana na kin jini gwamnatin mulkin sojin kasar Birma. Wani kakakin ma´aikatar harkokin waje ya nunar da cewa a kullum ministan harkokin wajen Jamus F.-W. Steinmeier na goyon baya aiwatar da canje canje a Birma tare da yin wata tattaunawar sulhu tsakanin gwamnatin mulkin soji da masu neman sauyi. A yau ma dai dubun dubatan sufaye da fararen hula sun ci-gaba da macin kyamar gwamnati a babban birnin kasar Rangoon, kwana na 7 a jere. Kawo yanzu zanga-zangar na tafiya cikin lumana amma ana kara nuna fargabar cewa dakarun tsaro ka iya murkushe ta. Soe Aung na wata kungiyar ´yan majalisar dokokin Burma wanda ke gudun hijira a Thailand ya ce al´umar kasar na kara samun karfin guiwar nuna adawa da gwamnati.

Soe Aung:

“Ya zama wajibi gwamnatin mulkin sojin ta san cewa ba zata ci-gaba da mulki har abada ba. Dole ne ta sasanta da jama´a dole ne kuma ta sasanta da sauran shugabannin siyasa.”