1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Le Pen ta kaddamar da takarar shugabancin Faransa

Yusuf Bala Nayaya
February 5, 2017

Magoya bayan na Marine Le Pen sun yi ta tururuwa zuwa babbar cibiyar taron jam'iyyarsu a birnin Lyon a Faransa a wannan rana ta Lahadi da ke zama rana ta biyu ta taron jam'iyyar ta National Front.

https://p.dw.com/p/2X0rO
Frankreich Wahlkampf Front National Marine Le Pen
Hoto: Reuters/R. Pratta

'Yar takarar shugabancin Faransa karkashin jam'iyyar masu adawa da baki a Faransa Marine Le Pen ta bayyana cewa matakin da Birtaniya ta dauka na ficewa daga Kungiyar Tarayyar Turai da zaben Shugaba Donald Trump a matsayin shugaban Amirka wadannan dalilai ne za su sanya al'ummar Faransa su yi zabe dan samun sauyi.

Magoya bayan na Le Pen sun yi ta tururuwa zuwa babbar cibiyar taron jam'iyyarsu a birnin Lyon a Faransa a wannan rana ta Lahadi da ke zama rana ta biyu ta taron jam'iyyar ta National Front mai adawa da yawaitar baki a Faransa. Le Pen za ta yi jawabi kan abubuwa 144 da ta sanya a gaba na kokarin zama shugabar Faransa da suka hadar da batun Kungiyar EU da NATO.