Lauran Bagbo ya kai ziyara a wasu yankuna na ƙasar Cote d´Ivoire
May 8, 2006Shugaban ƙasar Cote d´Ivoire Lauran Bagbo, ya kai ziyara aiki a wasu sassa na ƙasa.
A jawabin da yayi, shugaban yi suka da kakkausar halshe, ga masu buƙatar kiffar da shi, daga karagar mulki.
A fakaice, Lauran Bagbo, ya nuna cewar tawagogin shiga tsakanin na ƙasa da ƙasa na nuna son zuciya a ayyukan da su ke gudanarwa.
Manazarta harakokin siyara a Cote D´Ivoire ,na danganta wannnan kalamomi, da wani mataki na maida hannun agogo baya, ga yunƙurin cimma zaman lahia a wannan ƙasa, da ke fama da rikicin tawaye da na siyasa.
A nasa ɓangare jiya ne, ta kamata Praministan riƙwan ƙwarya Charles Konnan Banny, ya koma gida Abijan, bayan ziyara aiki da ya kai a ƙasashen turai , to saidai, a wani mataki na ba zata, a ka bayyana ɗagewar komawar, bisa dukkan alamu, a dalili da martakan tsaro.