Kwamtin sulhu ya yi taron gaggawa akan halin da ake ciki a Libanon
July 14, 2006Talla
Kwamitin sulhu na MDD ya yi wani taron gaggawa akan halin da ake ciki a Lebanon a daidai lokacin da Isra´ila ta sake kai harin bam akan filin jirgin saman birnin Beirut kwana na biyu a jere. A lokacin da yake magana a hedkwatar MDD dake birnin New York mai kula da harkokin ketare na Lebanon Nouhad Mahmoud yayi tir da hare haren sannan yayi kira da a kawo karshen farmakin da jiragen saman yakin Isra´ila ke kaiwa kasar sa. Shi kuwa jakadan Isra´ila a MDD Dan Gillermann ya kare matakin sojin na Isra´ila ne yana mai cewa ta na mayar da martani ne kai tsaye ga wani yaki da aka kaddamar a kan ta. Jakadan Amirka a MDD John Bolton ya ce Washington ta damu game da yiwuwar rugujewar demukiradiya a Lebanon da kuma aikace aikacen kungiyar Hezbollah da ka iya haddasa rashin zaman lafiya a kasar.