Kwamitin sulhu ya yi tir da harin da aka kai kan sojojin AU a Darfur
October 3, 2007Kwamitin sulhu na MDD ya yi tir da mummunan harin nan na karshen mako wanda ya halaka sojoji 10 na rundunar kiyaye zaman lafiya ta KTA AU a lardin Darfur na kasar Sudan. Bayan wata tattaunawa ta kwanaki biyu, jakadan Ghana a MDD Leslie Christian wanda ke jagorantar kwamitin sulhu a wannan wata ya karanta wata sanarwar wadda ta yi tir da harin wanda ake zargin ´yan tawaye da hannu a ciki. MDD ta bukaci a yi duk iya kokarin cafke wadanda suka aikata wannan ta´asa don a gurfanad da su gaban shari´a. Kwamitin sulhu mai membobi kasashe 15 ya ce harin ya zo ne a daidai lokacin da ake shirin gudanar da taron sulhu a Libya a ranar 27 ga watan nan na oktoba. Yayi gargadin cewa ba za´a amince da duk wani yunkuri na yiwa kokarin samar da zaman lafiya a Darfur yankan baya ba.