1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwalambiya: Za a fara binciken 'yan FARC

Abdul-raheem Hassan
March 15, 2018

Hukumomin shari'a za su fara bincike domin fara shari'a kan laifukan yaki da ake zargin 'yan tawayen FARC da aikatawa a yakin basasar da aka kwashe sama da shekaru 50 ana yi.

https://p.dw.com/p/2uPaf
Kolumbien Rosen-Logo der FARC Partei
Hoto: ANNCOL

A wani mataki na cimma yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin gwamnatin Kwalambiya da 'yan tawayen FARC, gwamnati ta fidda shirin da zai ba wa wadanda yakin ya shafa damar gabatar da kara. Sai dai ba'a tsaida lokacin fara sauraron ba'asin kararrakin da za a gabatar a gaban kotu ba.

Tun bayan da gwamnatin Kwalambiya ta cimma yarjejeniyar zaman lafiya da 'yan tawayen FARC a shekarar 2016, sama da tsoffin 'yan tawayen dubu 4,700 sun amince da ba wa kotun hadin kai wajen amsa laifukan su domin jajantawa wadanda abin ya shafa. Akalla mutane dubu 250,000 aka kiyasta suka mutu a yakin basarar kasar yayin da wasu dubu 60 suka bace babu labari.