1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwalambiya ta nemi dauki kan 'yan hijira

Yusuf Bala Nayaya
May 11, 2018

Shugaban kasar Kwalambiya Juan Manuel Santos ya bayyana kwararar 'yan gudun hijira da ke shiga kasarsa daga Venezuela me fama da rikici a matsayin "abin ta da hankalin al'umma".

https://p.dw.com/p/2xYNf
Kolumbien Migranten aus Venezuela
Hoto: Getty Images/AFP/G. Castellanos

Shugaba Juan Manuel Santos ya yi kira ga al'ummomin kasa da kasa da su kai masu dauki. Ya fada wa kamfanin dillancin labaran Jamus na dpa cewa ba su saba da karbar 'yan gudun hijira da yawa haka ba. Ya ce suna tare da al'ummar Venezuela amma ban da gwamnati da ke jefa al'ummarta cikin hali na kaka na ka yi.

Rikici na siyasa da tattalin arziki shi ya sanya al'ummar ta Venezuela ke yin kaura zuwa Kwalambiya kamar yadda jami'an kula da shige da fice a Kwalambiya suka bayyana a Bogota inda suka ce fiye da 'yan Venezuela 650,000 ne ke rayuwa a Kwalambiya, kasar da ke da al'umma miliyan 49.