1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar Tarayyar Turai (KTT) Zata Fara Shawarwarin Karbar Turkiyya

December 17, 2004

A taron kolinsu da suke gudanarwa a Brussels shuagabannin kasashen KTT sun amince da gabatar da shawarwarin karbar Turkiyya a kungiyar daga uku ga watan oktoban shekara ta 2005

https://p.dw.com/p/Bve6
P/M Turkiyya Tayyib Erdogan a babbar mashawartar KTT
P/M Turkiyya Tayyib Erdogan a babbar mashawartar KTTHoto: AP

Bisa ta bakin P/M Turkiyya Tayyib Erdogan dai har yau da sauran rina a kaba, domin kuwa kamar yadda majiyoyi masu nasaba da mashawartan Turkiyyar suka nunar, kasar ba zata yarda da amincewa da ikon cin gashin kan bangaren Girkawa na tsuburin Cyprus, a matsayin sharadin gabatar da shawarwarin karbarta a Kungiyar Tarayyar Turai ba. Shugaban gwamnatin Jamus Gerhard Schröder, wanda ke ba da cikakken goyan baya ga karbar Turkiyyar a Kungiyar Tarayyar Turai bayan shekara ta 2014, ya bayyana fatan cimma bakin zaren warware matsalar ta Cyprus. A lokacin da yake bayani Schröder karawa yayi da cewar:

Maganar, a hakika, ba ta shafi amincewa da Cyprus ba ne a hukumance, batu ne da ya shafi shigar da ita a yarjejeniyar fito dake tsakanin Turkiyya da KTT. A saboda haka na sikankance cewar za a samu wata kafa, wacce zata gamsar da dukkan bangarorin biyu.

A taron kolinsu da suke gudanarwa yanzu haka a Brussels, shuagabannin kasashen Kungiyar ta Tarayyar Turai, sun amince da fara shawarwarin karbar Turkiyya a tutar kungiyar da kuma karfafa dangantakar kasar idan har shawarwarin, wadanda za a tafiyar da su ba tare da fayyace ainifin sakamakonsu ba, ba su cimma nasara akan manufa ba. Wannan bayanin ko da yake ya gamsar da ‚yan mazan-jiya dake dari-dari da karbar Turkiyyar a KTT, amma ita kanta kasar ta yi kakkausan suka game da shi, da kuma shawarar kungiyar na kayyade yawan ‚yan ci rani Turkawa da za a kyalesu su rika neman aiki a sauran kasashenta bayan karbar Turkiyyar. Tuni dai P/M kasar Sweden Gunnar Persson ya gargadi Turkiyyar a game da neman wuce gona da iri a bukatun da take neman shimfidawa. A sakamakon kai ruwa ranar da aka sha famar yi a game da kasar ta Turkiyya, ba a mayar da hankali sosai ga ganawar da aka shirya tsakanin sakatare-janar na MDD Kofi Annan da shuagabannin kasashen KTT ba, inda zasu tattauna manufofin hadin kai da ma’amalla tsakanin sassan biyu. An dai shiga yada jita-jita a game da ko shin Kofi Annan zai iya shiga tsakanin domin shawo kan matsalar ta Cyprus. A cikin watan afrilun da ya wuce ne Girkawan Cyprus suka yi fatali da shawarar da Kofi Annan ya bayar na sake hadewar tsuburin bayan rarrabuwa ta tsawon shekaru 30, a yayinda a daya bangaren Turkawan tsuburin suka amince da shawarar tasa.