1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar kasashen Musulmi OIC tayi kira ga dakatar da zubda jini a Iraqi

November 25, 2006
https://p.dw.com/p/BuaN

A halin da ake ciki kuma kungiyar kasashen musulmi ta duniya tayi kira da dakatar da zubda jini tsakanin yan sunni da yan shia a Iraqi,tana mai tunatarwa shugabannin addini na kasar alkawura da suka dauka na hana zubda jinin musulmi.

A daya hannun kuma wani jamiin kungiyar kasashen larabawa a birnin Alkhahira yace ana sa ran ministocin kasashen wajen kungiyar mai membobi 22 zasu gana a birnin Alkhahira a ranar 5 ga watan disamba inda zasu yi kira ga bangarorin dake yaki da juna a Iraqi dasu kawo karshen yawan zubda jini a kasar.

Sakataren kungiyar kasashen musulmi Ekmaleddin Ihsanoglu yace ya kamata shugabbanin addini na Iraqi wadanda sukayi rantsuwa a dakin Kaaba ba zasu zubda jinin yan uwansu musulmi da suji tsaron Allah su dakatar da wannan balai.

A dai ranar 20 ga watan oktoba ne shugabanin addinin na Iraqi sukayi kira ga magoya bayansu da su dakatar da fada tsakaninsu.