1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar EU ta nuna fargabar kazancewar rikicin Gabas ta Tsakiya

July 14, 2006
https://p.dw.com/p/Buqb
A halin da ake ciki KTT ta nuna fargabar cewa hare haren da Isra´ila ke kaiwa Lebanon ka iya janyo kasar Syria cikin mummunan fadan da ake yi. Ministan harkokin wajen Finland, kasar da ke rike da shugabancin karba-karba na kungiyar EU, Erkki Toumioja ya ce idan haka ya faru to ba wanda ya san karshen rikicin. A lokaci daya ministan ya sanar da cewa a gobe asabar babban jami´in harkokin ketare na EU Javier Solana zai fara rangadin yankin GTT a wani yunkuri na yin sulhu. Shi kuwa shugaban Iran Mahmud Ahmedi Nijad ya yiwa Isra´ila kashedi ne da kada ta kuskura ta kaiwa Syria hari. Yace yin haka tamkar kaddamar da yaki ne akan dukkan kasashen musulmi.