1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun Ruwanda ta karbi karar 'yan adawa da tazarce

Gazali Abdou tasawaSeptember 9, 2015

Kotun kolin kasar ta tabbatar da halalcin karar da 'yan adawa suka shigar don kalubalantar shirin yi wa kundin tsarin milki kwaskwarima domin tazarcen Kagame

https://p.dw.com/p/1GTiH
Paul Kagame Präsident Ruanda
Hoto: picture-alliance/dpa

Kotun kolin Ruwanda ta bayyana halarcin karar da wata jam'iyyar adawar kasar ta shigar a gabanta ta na mai kalubalantar yunkurin Shugaba Paul Kagame na yi wa kundin tsarin milkin kasarsa kwaskwarima domin sake tsayawa takarar neman shugabancin kasar a karo na ukku.

Tuni kotun wacce ta bayyana wannan matsayi nata ta kuma tsaida ranar 23 ga wannan wata na Satumba a matsayin ranar da za ta bude zaman shari'a kan wannan batu.

Tun a cikin watan Yulin da ya gabata ne dai majalissar dokokin kasar ta Ruwanda ta kada kuri'ar amincewa da bukatar shugaba Paul Kagame wacce za a gudanar da zaben raba gardama a kanta a nan gaba a kasar domin bashi damar yin tazarce a kan karagar milkin kasar a wani sabon wa'adin na shekaru bakwai.

A makon da ya gabata dai kasar Amirka ta bayyana adawarta da wannan shiri na shugaba Kagame