1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun Najeriya ta wanke Saraki

June 14, 2017

Kotun da'ar ma'aikata ta wanke shugaban majalisar dattawan Najeriya Sanata Bukola Saraki, kan zargin boye gaskiyar kadarorin da ya mallaka.

https://p.dw.com/p/2ei4V
Nigeria Bukola Saraki
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

An dai fara shari'a da Saraki watanni shida da darewarsa kujerar shugabancin majalisar, kafin daga bisani aka kwashe sama da shekara guda ana shari'ar a Kotun da'ar ma'aikatar kasar.

Alkalin kotun mai shari'a Danladi Umar, ya bayyana cewa lauyoyin gwamnatin Najeriya da ke tuhumar wanda aka zarga a shari'ar, sun gaza gamsar da kwararan hujjoji da zai tabbatar da zargin laifin da ake wa Saraki.

A ranar 4 ga wannan watan Yunin ne, shugaban majalisar dattawan Najeriyar ya shigar da karar da ke bukatar wanke shi daga laifin da ake tuhumarsa akai.