1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun ICC za ta binciken cin zarafin dan Adam a Burundi

Gazali Abdou Tasawa
November 9, 2017

Kotun hukuntan manyan laifuka ta kasa da kasa ta ICC ta ba da izinin aiwatar da bincike kan zargin cin zarafin dan Adam a Burundi daga ranar 26 ga watan Aprilun 2015 zuwa ta 26 ga watan Oktoban 2017. 

https://p.dw.com/p/2nNbY
Burundi Symbolbild Ermittlungen Internationaler Strafgerichtshof
Hoto: picture-alliance/AP Photo/J. Delay

Kotun ta ICC ta sanar da wannan mataki nata ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan Alhamis inda ta ce binciken zai shafi laifukan da suka hada da na kisa da azabtarwa da fyade da dai sauran laifukan cin zarafin dan Adam da aka aikata a cikin kasar ta Burundi ko kuma wadanda 'yan asalin kasar suka aikata a wasu kasashen ketare. 

Wasu alkalumma da kotun ta ICC ta wallafa sun nunar da cewa mutane akalla dubu da 200 suka halaka a yayin da wasu sama da dubu 400 suka shiga gudun hijira a cikin rikicin siyasar da ya barke a kasar ta Burundi a sakamakon tazarcen Shugaba Nkurunziza. A watan Oktoban da ya gabata ne dai kasar Burundi ta kasance kasa ta farko da ta fice daga kotun ta ICC a hakumance.