1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta halasta wa Najeriya kudaden da aka gano a Legas

Abdul-raheem Hassan
June 6, 2017

Wata babbar kotun tarayyar Najeriya ta umarci a maiyar wa gwamnatin kasar makudan kudaden da aka gano a wani gida da ke Legas, kudin da yawansu ya kai dalar Amirka miliyan 43 ba tare sanin hakikanin masu shi ba.

https://p.dw.com/p/2eDAU
Bündel von US Dollarnoten Symbolbild Geld Währung Geldscheine
Hoto: picture-alliance/John Greve

Mai shari'a Muslim Hassan da ya yanke hukuncin, ya ce kudaden ba a kai ga samun kwararan shaidu a kan wanda ya mallakesu da kuma abinda ake da niyar aikatawa da su ba. A watan Afrilu na wannan shekara ne hukumar yaki da cin hanci da masu yi wa tattalin arziki zagon kasa EFCC ta bankado kudaden a cikin wani gida da ke a Legas.

A baya dai hukumar leken asiri ta kasar NIA, ta yi ikirarin kudaden mallakan hukumar ce da niyar gudanar da wasu aiyuka a tsohuwar gwamnatin tsohon shugaba Goodluck Jonathan. Bankado wannan badakalar ce ya sa gwamnati ta dakatar da shugaban hukumar leken asirin kasar don a gudanar da bincike.

Kawo yanzu dai ba a kai ga gabatar da rahoton bincike na kwamitin da aka nada su gudanar da bincike a kan shugaban hukumar da ya alakanta kansa da wadannan makudan kudade ba.