Kokarin shawo kan matsalar bakin haure
November 22, 2006Talla
A yau aka bude taron wuni biyu , a tsakanin wakilan kungiyyar Eu dana kasashen Africa, a can birnin Tripoli na kasar Libya.
Taron , wanda ke zaman irin sa na farko, zai mayar da hankali ne kann matsalolin bakin haure daga kasashen Africa izuwa nahiyar turai.
Ana dai sa ran a karshen taron wuni biyun, mahalarta taron zasu fitar da yarjejeniya da suke fata ta zama ta karshe, a kokarin dakile wannan matsala da taki ci taki cinyewa