1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin murkushe 'yan jarida a Turkiya

Lateefa Mustapha Ja'afar
February 27, 2017

Bayan kwashe tsahon kwanaki 13 a kwamar jami'an 'yan sandan Turkiya, dan jaridar nan na Jamus Deniz Yucel ya gurfana a akron farko a gaban kuliya.

https://p.dw.com/p/2YLsv
 Deniz Yucel dan jaridar Jamus da mahukuntan Turkiya suka tsare
Deniz Yucel dan jaridar Jamus da mahukuntan Turkiya suka tsareHoto: picture-alliance/Eventpress

Jaridar Die Welt ta Jamus wadda a nan ne Yucel kewa aiki yayin da 'yan sanda suka cafke shi a Turkiyan, ta tabbatar da gurfanar tasa a gaban kuliya. Yucel dai na rike da fasfo biyu na kasashen Jamus da Turkiya, kuma yana zaman dan jaridar Jamus na farko da jami'an 'yan sandan na Turkiya suka tsare a wani bangare na kokarin murkushe 'yan jaridu da kasar ke yi, tun bayan da mahukuntanta suka sanya dokar ta baci sakamakon yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba da ta fuskanata a shekarar da ta gabata ta 2016.