KOFI ANAN YA AMINCEWA DA BUKATAR AMURKA DA IRAQI...
January 27, 2004Bisa rahotanni da zarar jamian na mdd sun koma kasar ta iraqi zasu kalailaice yanayin dake faruwa ne a fadin kasar ta iraqi baki daya don duba yiwuwar gudanar da zabe kafin nan da 30 ga watan yuni na wan nan shekara da muke ciki. MDD dai a baya ta janye jami,an nata ne daga kasar ta iraqi a ranar 19 ga wata agusta na shekarar data gabata sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai a babban ofishin ta dake birnin Bagadaza,wanda sakamakon hakan mutane 22 suka rugamu gidan gaskiya ciki har da jakadan majalisar na musanman a kasar ta iraqi.
Jim kadan dai bayan wadan nan kalamai na Anan sojojin taron dangi´bisa jagorancin kasar Amurka suka ce kalaman na Anan sunzo a dai dai lokacin da ake da bukatar su,domin a nasu ganin hakan zai taimaka wajen dankawa yan kasar ta iraqi mulkin su a hannun su ta hanyar gudanar da zabe a kasar.
Bisa hakan kuwa sojojin taron dangin sun tabbatar da cewa a nasu bangaren zasuyi duk iya bakin kokarin su na ganin an samu kwanciyar zaman lafiya a kasar ta iraqi don ganin kwalliya ta biya kudin sabulu dangane da wan nan mataki da ake kokarin dauka. Bugu da kari a daya hannun kuma shugaban darikar shi,awa na kasar ta Iraqi Ali Al sistani ya tabbatar da cewa muddin jamian mdd suka gudanar da aikin su a kasar ta iraqi kamar yadda ya dace,kuma suka ce zabe ba zai yiwu ba to babu shakka zai amince da hakan shi da alummar sa baki daya.
A dai tun can baya ministan harkokin cikin gida dake cikin gwamnatin wucin gadi ta kasar,wanda dan kabilar shi,awa ne,wato Nuri Badran ya fada cewa gudanar da zabe a kasar ta iraqi a halin da ake ciki yanzu ba zai yiwuba a sabili da rashin tsaro da kuma rikice rikice dake faruwa a kai a kai.
A wata sabuwa kuma,duk da aiyukan kiyaye zaman lafiya da sojojin taron dangi keyi a kasar ta iraqi,har yanzu tashe tashen hankula naci gaba da gudana a yankuna daban daban na cikin kasar.
Na baya bayan nan kuwa shine na mutuwar wasu yan sandan kasar su bakwai,sakamakon musayar wuta da sukayi da yan fadan sari ka noke a ranar lahadin data gabata.
Sai kuma na rasa rayukan wasu sojojin Amurka biyu da farar hula daya da akayi sakamakon hatsarin da wani karamin jirgin saman na Amurka yayi a arewa da birnin Mosul.