1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jagoran addini na Iran ya gargadi 'yan majalisa

Kamaluddeen SaniMay 28, 2016

Babban jagoran koli na addinin Islama na kasar Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bukaci sababbin 'yan majalisar dokokin kasar da aka rantsar da su yi taka tsan-tsan da kasashen yamma.

https://p.dw.com/p/1IwVQ
Iran Teheran Ayatollah Ali Khamenei (C)
Hoto: Imago/Xinhua

Ta cikin wani sako da ya aika wa sababbin 'yan majalisar, jagoran ya ce yanayin tsarin kasa da addini da kuma yadda al'umomin kasa da kasa ke kallon su cike da barazana yasha ban-ban da yadda kasar take ada. Ayatollah Ali Khamenei wanda shi ne ke yanke hukunci na karshe ga dukkan wasu muhiman batutuwa da suka tunkaro a kasar, ya kuma kara jaddada kiransa daya saba na ci gaba da yin biyayya ga dukkan tanade-tanden dokokin juyin-juya hali na shekara ta 1979 gami da nuna tirjiya ga dukkan wasu bakin al'adu na kasashen yammacin duniya.