1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kenya: Binciken rantsar da Raila Odinga

Zainab Mohammed Abubakar
January 31, 2018

Gwamnatin Kenya na binciken rantsar da kansa da madugun 'yan adawar Kenya ya yi, domin nazarin ko hakan ya cancanci daukar matakin hukunci a kansa.

https://p.dw.com/p/2rqGq
Raila Odinga
Hoto: Getty Images/AFP/Y. Chiba

A jiya Talata ne dai, Odinga ya rantsar da kansa a matsayin shugaban jama'a a birnin Nairobi a bainar dubban magoya bayansa, bisa ikirarin gwamnatin Uhuru Kenyatta haramtacciya ce.

Sanarwar gwamnati na bayyana matakin na jiya, a matsayin yunkurin kifar da zababbiyyar gwammatin Janhuriyar Kenya. Gabannin bukin rantsar da Odinga dai, babban Alkalin Kenyan ya yi gargadin cewar, wannan yunkuri tamkar cin amanar kasa ce.

Ya zuwa yau Laraba dai wasu gidajen talabijin masu zaman kansu na cigaba da zama a rufe, matakin da gwamnati ta ce na bangaren binciken da take gudanarwa dangane da yayata rantsar da madugun 'yan adawar.