1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kawo karshen yakin a Kwalambiya

A'Raheem HassanJune 24, 2016

Gwamnatin Kwalambiya da kungiyar 'yan tawayen kasar ta FARC, sun sanya hannu a yarjejeniyar kawo karshen yakin mafi dadewa a Latin Amirka.

https://p.dw.com/p/1JCaz
Kuba Raul Castro, Juan Manuel Santos und FARC-Rebellenführer Rodrigo Londono in Havanna
Hoto: picture-alliance/dpa/EPA/A. Ernesto

Wannan lamari dai ya dasa kyakkyawar fata a zukatan al'ummar kasar na ganin kasar na dab da samun kwanciyar hankali da zaman lafiya. Sanya hannu a kan yarjejeniyar ajiye makaman mayakan FARC dai ya tanadi shirin tattara mayaka a wuri guda har na tsawon watanni shida da fara aikin yarjejeniyar.

Shugaban Kwalambiya Juan Manuel Santos da jagoran 'yan tawayen Timoleon Jimenez suka ce suna fatan yarjejeniyar za ta kawo karshen yakin da kasar ke fama da shi sama shekaru 50.

Rahotanni na nuni da cewar, duk da farin cikin da al'ummar kasar ke ciki, akwai fargabar yiwuwar bullar wata kungiyar 'yan tawaye da za ta maye gurbin mayakan juyin juya halin na FARC.