Kawar da muggan makamai
September 23, 2010Talla
Wasu ƙasashe goma masu faɗa aji, sun fara wani taro don kawar da makaman nukiliya a duniya. ƙasashen waɗanda ke taron a ƙarƙashin jagorancin Jamus da Japan da Ostaraliya, suna taron na su ne a gefen inda ake taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York. Ministan harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle yace, samun duniyar da bata da makaman nukiliya wani mahimmin abune ga muhallin duniya. Inda ya yi gargaɗin cewa, in ba'a ɗau matakai ba, to makaman nukiliya za su iya shiga hannun 'yan ta'adda. ƙasashen goma za su sake ganawa a birnin Berlin a wata ranar da ba'a kai ga bayyanawa ba izuwa yanzu.
Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Umaru Aliyu