Kasa ta halaka rayuka a Kwango
August 17, 2017Talla
Wani ibtila'in zaftarewar kasa ya halaka akalla mutane 40 a lardin Ituri da ke a jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango. Wani mataimakin gwamnan lardin ya ce lamarin ya auku ne bayan ruwan sama mai karfi da aka tabka a wani kauyen da galibi masunta ke zaune a cikinsa.
Lamarin na faruwa ne yayin da a Freetown babban birnin kasar Saliyo kuwa, aka shiga rana ta biyu ta zaman makoki tare da binne daruruwan mutanen da ambaliya ta halaka a ranar Litinin da ta gabata.
Akwai wasu sama da mutum 600 da suka bace har kuma ya zuwa yanzu babu labarinsu a bala'in na Saliyo. Tuni dai gwamnatin kasar ta yi yekuwar agajin kasashen duniya, don kai mata dauki a halin da ta tsinci kanta ciki.