1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasa ta halaka rayuka a Kwango

August 17, 2017

Wani sabon ibtila'in zaftarewar kasa ya yi sanadin mutuwar mutane 40 a lardin Ituri da ke a jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango, kamar yadda mahukuntan kasar suka tabbatar.

https://p.dw.com/p/2iPUx
Sierra Leone Freetown nach dem Erdrutsch
Hoto: Imago/Xinhua

Wani ibtila'in zaftarewar kasa ya halaka akalla mutane 40 a lardin Ituri da ke a jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango. Wani mataimakin gwamnan lardin ya ce lamarin ya auku ne bayan ruwan sama mai karfi da aka tabka a wani kauyen da galibi masunta ke zaune a cikinsa.

Lamarin na faruwa ne yayin da a Freetown babban birnin kasar Saliyo kuwa, aka shiga rana ta biyu ta zaman makoki tare da binne daruruwan mutanen da ambaliya ta halaka a ranar Litinin da ta gabata.

Akwai wasu sama da mutum 600 da suka bace har kuma ya zuwa yanzu babu labarinsu a bala'in na Saliyo. Tuni dai gwamnatin kasar ta yi yekuwar agajin kasashen duniya, don kai mata dauki a halin da ta tsinci kanta ciki.