Karawar Alƙa'ida da sojojin Moritaniya
September 18, 2010Sojojin ƙasar Moritaniya sun kara da 'yan ƙungiyar Alƙa'ida a kusa da iyaka da ƙasar Mali, a dai-dai lokacin da ake zargin ƙungiyar da sace wasu ma'aikatan baƙi a ƙasar Nijar. Wani kakakin sojojin Moritaniya ya ce dakarunsu sun hallaka 'yan Alƙa'ida 12 a wani gumurzu da aka yi, kana suma sojojin sun rasa mutane biyu. Tun a jiya dai jami'an tsaron ƙasar Aljeriya su ka ce ana wata fafatawa tsakanin sojin Moritaniya da 'yan tsagerun Alƙa'ida da ke arewacin Afirka. Dakarun Moritaniya cikin motoci kimanin 20 su ka shiga faɗan a kilomita 100 daga birnin Timbuktu na ƙasar Mali. Ba'a dai bayyana cewa ko wannan karawa ta na alaƙa da sace turawan Faransa da aka yi a jamhuriyar Nijar ba. Jami'an tsaron Aljeriya suka ce waɗanda suka sace turawan Faransa biyar da wasu mutane biyu 'yan ƙasashen Togo da Madagaska a yankin Arlit dake jamhuriyar Nijar, sun tsallaka da su cikin hamadar ƙasar Mali.
Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Yahouza Sadissou Madobi