1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jirgin ruwa ya kife da 'yan Rohingya

Abdul-raheem Hassan MNA
October 9, 2017

Mutane 12 sun mutu yayin da jirgin ruwa makare da Musulman Rohingya da ke tserewa zuwa Bangledesh ya nitse a ruwa. Hukumomin kula da gabar ruwan sun ce cikin gawarwakin akwai kananan yara guda biyar.

https://p.dw.com/p/2lU7k
Bangladesch Rohingya-Muslime in einem Boot
Hoto: picture-alliance/ZUMA Wire/Zakir Hossain Chowdhury

Rahotanin 'yan sanda na cewa cikin mutane 35 da ke cunkushe a cikin kwale-kwalen, mutane takwas kadai suka tsira da kyar. To sai dai masu ayyukan ceto a ruwan sun ce babu tabbacin adadin mutanen da suka bata a cikin ruwan kawo yanzu.

Tun bayan barkewar rikicin kabilanci a yankin na Rohingya a watan Agusta, dubban 'yan yankin ke gudun hijira a makociyar kasar wato Bangledesh. Kamarin rikicin ne dai ya sa gwamnatin Bangledesh jaddada matakan tana ci gaba da ba wa 'yan Rohingyan mafaka da kayan agaji. Amma sun gargadi gwamnatin kasar Myanmar da su dau matakan gaggawa da zai kawo karshen rikicin don a samu a maido da 'yan gudun hijiran kasar da ke galabaita.