1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Japan za ta shirya gasar Olympics ta 2020

September 8, 2013

'Yan ƙasar Japan na ci gaba da kasancewa cikin farin ciki da murna bayan da kwamitin wasannin Olympic na duniya IOC ya zaɓi Tokyo a matsayin birnin da zai karɓi baƙuncin wasanin.

https://p.dw.com/p/19dgv
©Kyodo/MAXPPP - 30/05/2013 ; TOKYO, Japan - The numbers "2020" are displayed on Tokyo Tower on May 30, 2013, marking 100 days before the venue of the 2020 Summer Olympics is decided. The Japanese capital is one of three candidate cities, along with Istanbul and Madrid. (Kyodo)
Hoto: picture-alliance/dpa

Jacques Rogge shugaban kwamitin wasannin na Olympics shi ne ya bayyana sunan ƙasar ta Japon a matsayin ƙasar da za ta tsara wasanin a wani zaman taron da kwamitin na Olympics ɗin ya yi a Buenos Aires. A ƙarshen ƙidayar ƙuri'un da aka yi birnin Tokyo ya samu kuri'u 60, kana Istanbul na da 36, bayan tun da farko dai an riga aka fitar da birnin Madrid tun a zagayen fari.

Wannan dai shi ne karo na biyu da ƙasar ke shirya wasannin bayan wanda ta tsara a shekara ta1964,sai dai kuma a ƙasashen Spain da Turkiya waɗanda suka sha kaye a takarar an yi tsit kamar a yin mutuwa.Tun da farko dai an yi tsamanin Japan ɗin ba za ta samu nasarar ba saboda lamarin da ya afku a ƙasar a shekara ta 2011 na hatsarin tashar nukiliya ta Fukushima.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman