1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus zata kula da gabar tekun Libanon yadda ya kamata inji Steinmeier

September 8, 2006
https://p.dw.com/p/BukI
Duk da sabbin sharudda da gwamnati a birnin Berlin ta gindaya, ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier ya yi fatan girke sojojin ruwan Jamus a gabar tekun kasar Libanon. Bayan tattaunawar da yayi da FM Libanon Fuad Siniora a birnin Beirut, Steinmeier ya ce za´a kula da yankunan ruwan kamar yadda aka amince tsakanin MDD da kuma Libanon. Sojojin ruwan na Jamus zasu sa ido don hana yin sumogar makamai zuwa ga mayakan Hisbollah. A dai halin da ake cikin Steinmeier ya isa birnin Kudus inda zai gana da takwararsa ta isra´ila Zipi Livni. A jiya alhamsi Isra´ila ta janye kawanyar da ta yiwa iyakokin sama na Libanon, amma ta na ci-gaba da toshe iyakokin ruwa sabanin sanarwar da ta bayar a ranar laraba. Gwamnati a birnin Kudus ta ce sai dakarun kasa da kasa sun isa yankin ne sannan zata kammala janyewar.