Jamus ta cirawa Mr Musharraf tuta
November 28, 2007Talla
Jamus ta yi maraba da matakin shugaba Musharraf na ajiye kakinsa na soji. Matakin a cewar ministan harkokin waje na ƙasar, Frank Walter Steimeir abune da zai sanar da kyakkyawan yanayi, na gudanar da zaɓe mai tsafta a ƙasar. Mr Staeinmeir ya kuma buƙaci Pakistan cire dokar ta ɓacin da ta ƙaƙaba a ƙasar. Yin hakan a cewar ministan zai taimaka wajen cimma burin da ƙasar ta sa a gaba na komawa tafarki na mulkin Dimokruɗiyya. A ranar 8 ga watan Disambar shekara ta 2008 ne aka shirya yin zaɓen gama garin a Pakistan ɗin.