Jamus: Hadarin jirgin kasa ya kashe mutane
February 9, 2016Talla
Kamfanin dillancin labaran Jamus na DPA ya ce hadarin ya auku ne daidai lokacin da mutane suke tururuwa wajen tafiya aiki da sanyin safiyar yau Talata.
Masu aikin ceto suka ce baya ga wanda suka rasu, wasu mutanen da yawansu ya kai 150 sun jikkata inda wasunsu ke cikin hali rai kwakwai mutu kwakwai.
Tuni aka aike da jirage ceto masu saukar ungulu domin kwashe wanda ke cikin mawuyacin halin domin kaisu aisbiti don ceton ransu. Ya zuwa yanzu ba a tantance dalilin aukuwar hadarin ba.