1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: Demokradiyya ba ta fiskantar barazana

Yusuf Bala Nayaya
October 3, 2017

Ministan kudin Jamus mai barin gado ya bayyana cewa demokradiyyar Jamus ta yi girkuwar da ba za ta fiskanci wata barazana ba daga jam'iyyar masu kyamar baki ta AfD.

https://p.dw.com/p/2l8RL
Schäuble Kriminalstatistik 2008
Hoto: AP

Jam'iyyar ta AfD dai kawo yanzu ita ke zama jam'iyyar adawa ta uku mafi girma a majalisar dokokin Jamus.

Wolfgang Schaueble, da zai sauka daga mukamin ministan kudin na Jamus inda zai koma shugaban majalisar dokokin Jamus ya fadawa gidan jaridar Bild am Sonntag cewa,  jam'iyyar AfD me kyamar baki da ke sanya kafa a majalisar a karon farko da juyayyun manufofi ba za ta iya wani tasiri da ake fargabar za ta iya ba, kasancewar wasu abubuwan da suke muradi kundin tsarin mulkin Jamus ba zai ba su dama ba.

Schaueble dan shekaru 75 daga jam'iyyar 'yan Conservative ya karbi sabon mukamin ne bisa kwarin gwiwa da Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ke da shi a kansa yayin da jam'iyyarsu ta sanya shirin kawance da 'yan fafutikar kare muhalli ta Greens da 'yan gaba-gaba a kare manufofin kasuwanci Free Democrats wadanda za su iya neman mukamin na ministan kudi.