1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus da Faransa sun taka rawar gani kan batun Girka

Salissou BoukatriJuly 13, 2015

Ministocin harkokin wajan Faransa da Jamus sun ce irin huldar da ke tsakanin kasashen biyu ta taka rawar gani wajan cimma yarjejeniya kan batun kasar Girka.

https://p.dw.com/p/1FxuB
Frank-Walter Steinmeier da Laurent Fabius
Frank-Walter Steinmeier da Laurent FabiusHoto: picture-alliance/dpa/C. Rehder

Da ya ke magana a daura da taron tattaunawa kan nukiliyar kasar Iran a birnin Vienna, shugaban diflomasiyyar kasar Faransa Laurent Fabius ya ce, ya na mai tabbatar da cewa irin karfin huldar da ke tsakanin kasashen na Jamus da Faransa ce ta taimaka wajan kaiwa ga wannan matsayi, tare kuma da hada kan dukannin kasashen na Turai.

Shi ma daga nashi bengare Ministan harkokin wajan kasar Jamus Frank-Walter Steinmeier ya jaddada cewa, idan da babu kyaukyawar hulda tsakanin kasashen na Faransa da Jamus, da ba'a kai ga cimma wannan yarjejeniya kan kasar ta Girka ba. Kasashen na Turai dai sun amince da wata yarjejeniyar da zata bada damar sake wata tattaunawa don samar wa kasar ta Girka mafita a cikin wani tsari na tallafawa wannan kasa karo na uku bayan da aka shafe tsawon watanni shidda ana wannan tattaunawa.