Jammeh ya lashe zaben shugaban kasar Gambia da gagarumin rinjaye
September 23, 2006Talla
Shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh, wanda ya haye kan karagar mulki a wani juyin mulki da ya yi shekaru 12 da suka wuce, ya sake lashe zaben shugaban kasar da gagarumin rinjaye. Sakamakon karshe da hukumar zaben ta bayar dazu dazun nan a birnin Banjul, ya nunar da shugaba Jammeh ne ya yi nasara a wannan zabe, wanda rahotanni suka ce mutane ba su fita sosai don kada kuri´a ba. shugaba Jammeh ya samu da yawa daga cikin kuri´un da aka kada na mazabu 47 daga 48 a zaben na jiya juma´a. Tun da farko dai an yi hasashen cewa shugaban mai shekaru 41 a duniya zai lashe zaben, wanda kungiyoyin kare hakkin bil adama suka ce ba a kamanta dokoki na demukiradiya a ciki ba saboda tursasawa ´yan jarida da ´yan adawa.