1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jakadan Denmark ya bar Syria saboda dalilai na tsaro

February 11, 2006
https://p.dw.com/p/Bv8a

Denmark ta ce jakadanta da sauran ma´aikatan diplomasiyanta a Syria sun bar kasar saboda damuwa da ake da ita ta tsaron lafiyarsu. A makon da ya wuce masu zanga-zangar nuna fushi da buga zanen tozarta Annabi Mohammed SAW da wata jaridar Denmark ta fara yi, sun kona ofishin jakadancin kasar a birnin Damaskus. Ma´aikatar harkokin wajen Denmark ta ce ma´aikatan jakadancinta da aka sake tsugunar da su cikin wani otel, ba sa samun cikakkiyar kariya daga hukumomin Syria. A yau ma dai an ci-gaba da gudanar da zanga-zangar yin tir da cin mutuncin al´umar musulamai. A birnin Potiskum dake cikin jihar Yobe ta tarayyar Nijeriya an yi wata zanga-zangar lumana inda aka kona tutocin wasu kasashen Turai don nuna adawa da wannan batanci ga Manzon Rahma SAW. Wakilin mu a Chadi ma ya rawaito cewar a birnin Ndjamena ma an gudanar da irin wannan zanga-zanga a yau asabar.