Israila za ta gina sabbin gidaje
November 9, 2010Talla
Israila ta ce za ta cigaba da shirinta na gina wasu sabbin gidaje 1300 a yankunan larabawa da ta mamaye a gabashin birnin Kudus. Sanarwar ta ci karo da kalamai na baya bayan nan dake nuni da cewa Israilan za ta jinkirta gina sabbin matsugunan a gabashin kudus a wani mataki na wanzar da cigaban zaman lafiya da Falasdinawa. Hakan dai na faruwa ne cikin wani yanayi na tsaka mai wuya ga Firaministan Israilan Benjamin Netanyahu wanda a yanzu haka yake kasar Amirka domin tattaunawa akan hanyoyin farfado da shirin zaman lafiya a Gabas Ta Tsakiya. Wani mai magana da yawun gwamnatin Amirka ya baiyana matakin da cewa babban abin takaici ne da sosa rai.
Mawallafi : Abdullahi Tanko Bala
Edita : Umaru Aliyu