1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Tattalin arziki

Inganta sa'ar fawa

September 6, 2017

Sana’ar fawa tana daya daga cikin sana’o’in dake sama wa dimbin jama’a aikin yi a Najeriya. Sarkin Fawa na Najeriya Alhaji Hamisu Dan Gowon ya yi wa matasan kasar wani babban tanati na guraben ayyuka.

https://p.dw.com/p/2jQgq
Symbolbild Fleischindustrie Deutschland
Hoto: picture-alliance/dpa/B. Thissen

Shi dai Sarkin Fawar na Nigeria Alhaji Hamisu Dan Gowon mutum ne mai kaunar ganin matasa sun himmatu wajen neman na kai  musamman sana'a wadda sirrin arziki  ke cikinta. Don haka ne ya yi wa matasan tushe ta hanyar kafa musu kasuwar dabbobi da mayankunsu har ma da makaranta ta koyon sana'ar fawa.

 A wannan mayaka  da ya gina a Kano a kalla mutum  dubu biyar ake sa ran za su ci moriyarta sannan a kusa da ita akwai babbar kasuwar dabbobi.Alhaji Hamisu Dan Gowon  ya yi kira ga duk mai neman arziki  ya zo ya ci arzikin ya kuma bar arzikin a gurbinsa.

Ita wannan mayakan da aka yi wa gini na zamani  tana da wuraren adana nama da makarantu na Islamiyya da ta koyon sana'ar fawa kuma tun lokacin da aka aza harsashin gininta matasa suke gani a kasa.