1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Indiya ta kare matsayinta bisa sauyin yanayi

December 5, 2014

Kasar Indiya ta bayyana cewa ba za ta rattaba hannu ba kan duk wata yarjejeniya da za ta sanya ta rage iskar da take fitarwa mai gurbata muhalli.

https://p.dw.com/p/1Dzzw
Indien Stadt Mawsynram nassester Ort der Welt
Hoto: BIJU BORO/AFP/Getty Images

Prakash Javadekar mai fafutukar kare muhalli ya fadawa manema labarai a birnin New Delhi cewa, ba za su mika wuya ba kan duk wani abu da zai iya kawo zagon kasa ga ci gaban kasarsu.

Indiya ta bayyana wannan matsayin ne a wajen taron Majalisar Dinkin Duniya a Lima babban birnin kasar Peru, ta ce yunkurin na iya kawo nakasu ga ci gaban da ta ke samu, ya kuma kawo cikas ga fafutukar da ta ke yi na yaki da talauci a tsakanin al'ummarta.

Da yake jawabi yayin da yake barin taron na birnin Lima, Prakash Javadekar tsohon dan majalisa kuma mai fafutukar kare muhalli a kasar ta Indiya ya ce, ya je taron zuwa zuciyarsa a bude kuma ya gargadi tawagar Indiya cewa kasarsu ba zata daga kafa ba ko jin kunya idan za a zauna teburin zazzafar muhawara.

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Usman Shehu Usman