Hulɗa tsakanin Jamus da Turkiya
March 30, 2010A rana ta biyu ta ziyar da ta kai ƙasar Turkiya, shugabar gwamnatin Jamus Agela Merkel, ta ziyarci cibiyoyin al'adu da kasuwanci a ƙasar. Merkel ta kuma jaddada buƙatar inganta hulɗar musayar al'adu tsakanin ƙasashen biyu. Ta bayyana hakane ya yin da ta ziyarci wata makarantar jamusanci dake birnin Instanbul. Ƙasashen biyu yanzu haka suna yunƙurin kafa wata jami'ar haɗin gwiwa tsakaninsu, wanda za a kafa cikin ƙasar ta Turkiya. Yanzu haka abinda ake jira domin kafa wannan jami'ar shine amincewa majalisar dokokin Turkiya, abinda Merkel ta nuna fatar samun amincewa. Tun farko dai shugabar gwamnatin Jamus ta tattauna da Firimiyan ƙasar Tayyip Erdogan, inda suka taɓo batun shigar da Turkiya cikin Tarayyar Turai da kuma abinda ya shafi kafa makarantun harsunan Turkiya anan Jamus. Izuwa yanzu shugabar gwamnatin Jamus, ta ci gaba da nuna matsayin ta na yin adawa da shigar da Turkiya cikin EU, sai dai ta kasance abokiya ta musamman. 'Yan ƙasar Turkiya dai su suka fi ko wace ƙasa yawa a ƙasar Jamus
Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Yahouza Sadissou Madobi