1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukuncin kotun duniya a kan Charles Taylor

May 30, 2012

Tun a ranar 26 ga watan Afrilu kotun ƙasa da ƙasa ta birnin The Hague ta tabbatar da laifin yaƙi da cin zarafin bil Adama a kan tsohon shugaban na Laberiya.

https://p.dw.com/p/154H1
Former Liberian President Charles Taylor looks up to the public gallery as he waits for the start of his sentencing hearing in Leidschendam, near The Hague, Netherlands, Wednesday May 16, 2012. Taylor was to address judges personally during the sentencing hearing of his war crimes trial, asking for leniency even as he plans to appeal his conviction. In a landmark ruling in April, judges at the Special Court for Sierra Leone found Taylor guilty of 11 counts of war crimes and crimes against humanity, including murder, rape, and conscripting child soldiers. Judges at the U.N.-backed court said his aid was essential in in helping rebels across the border in Sierra Leone continue their bloody rampage during the West African nation's decade-long civil war, which ended in 2002 with more than 50,000 dead. (Foto:Evert-Jan Daniels, Pool/AP/dapd).
Hoto: AP

A wannan Laraba kotun ƙasa da ƙasa ta birnin The Hague take yanke hukunci a kan tsohon shugaban ƙasar Laberiya Charles Tayor wanda aka same shi da aikata laifin yaƙi. Babban alƙalin kotun musamman akan laifukan yaƙi da aka aikata a ƙasar Saliyo, Richard Lussick zai sanar da hukuncin. A ranar 26 ga watan Afrilu aka tabbatar da laifukan yaƙi da cin zarafin bil Adama a kan tsohon shugaban na Laberiya. Babbar mai shigar da ƙara ta kotun Brenda Hollis na bukatar a yanke wa Taylor hukuncin ɗaurin shekaru 80 a kurkuku. A cikin watan Maris aka kammala shari'ar da ake wa Taylor wadda aka ɗauki shekaru huɗu ana yi.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Usman Shehu Usman