Hukuncin haɗarin kamfanin Union Carbide.
June 7, 2010Wata kotu a ƙasar Indiya, ta yanke hukunci akan ta´asar da ta wakana yau shekaru 25 da suka gabata, a kamfanin gas na Union Carbide mallakar Amurika dake birin Bhopal na Indiya.
Ranar ukku ga watan Desemba na shekarar 1984 wasu tankokin gas suka farfashe a wannan kamfani, wanda suka yi sanadiyar mutuwar dubunan mutane.
Kotu tace wasu jami´an bakwai na kamfanin sun nuna sakaci, saboda haka ta yanke masu hukunci ɗaurin shekaru biyu tare da biyan tara ta Euro 1.800.
To sai dai wanda suka ƙetara rijiya da baya cikin wannan bila´i, da kuma Ƙungiyoyin kare haƙƙoƙin bani Adama, sun yi watsi da wannan hukunci wanda suka danganta da tsabar rashin adalci, saboda haka sun ɗaura ɗamara ci gaba da gwaggwarmaya, har sai an tabbatar da hukunci na gaskiya.
Mawwallafi: Yahouza Sadissou Madobi Edita: Abdullahi Tanko Bala