1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe mutane 16 a gabashin Nijar

Abdourahamane HassaneJuly 18, 2015

Mayaƙan Ƙungiyar Boko Harm sun kashe mutanen ne a harin da suka kai a wani ƙauyen da ke cikin BosSo a gabashin Diffa

https://p.dw.com/p/1G16s
Boko Haram Nigeria zerstörte Brücke
Hoto: DW/K. Gänsler

Hukumomin tsaro a Nijar sun tabbatar da cewar aƙalla mutane guda 16 suka mutu a harin da Boko Haram ta kai a wani ƙauyen da ke cikin Boso da ke a gabashin ƙasar cikin jihar Diffa.

Gidan telbijan mallakar gwamnati na Nijar ɗin ya ambato magajin garin Bosso Bako Mamadou,yana mai cewar mayaƙan sun buɗe wuta a lokacin harin na ranar Larba a kan wasu jama'ar a lokacin da suke cikin yin sallah. Nan take mutane 15 suka cikka kana ɗaya ya mutu sakamakon raunikan da ya samu daga bisani yayin da wasu huɗu suka jikkata.