1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumomin Nijar sun karfafa matakan tsaro tun bayan harin Agadez

May 31, 2013

Kungiyoyin fararan hula a Nijar na nuna damuwa ga matakan takaita walwala da tsananin bincike da jami'an tsaro su ka kaddamar a cikin manyan biranen kasar.

https://p.dw.com/p/18hqt
epa02847783 President Mahamadou Issoufou of Niger during a meeting with US President Barack Obama and fellow African leaders from Niger, Benin, and Guinea, in the Cabinet Room of the White House, in Washington DC, USA, 29 July 2011. EPA/MARTIN H. SIMON / POOL +++(c) dpa - Bildfunk+++
Mahamadou IssoufouHoto: picture alliance/dpa

A game da koken-koken kungiyoyin fararen hula kan karfafamatakan tsaro,ministan cikin gida na Nijar ya shirya wani babban taron gangami a birnin Yamai tare
da hadin gwiwar shugabannin hukumomin tsaro da wakillan al'umma domin yin baiyani game da dalillansu na daukar matakan da ma kuma neman goyan bayan al'umma a cikin aiwatar da wanann mataki.
Tun dai bayan abkuwar hare-haren ta'adancin da aka kai a jihar Agadez a makon da ya gabata, hukumomin tsaro su ka kara kaimi ga matakan tsaron da su ka dauka a baya, a kusan duk fadin
kasar a lokacin rikicin kasar Libiya da na Mali da ma na Boko-Haram Najeriya.Yanzu haka dai hukumomin tsaron sun kara baza
jami'an tsaro a cikin manyan biranan kasar, inda a gurare da dama su ka datse hanyoyi da binciken ababan hawa a bakin wasu ofisoshin dama a duk a wasu guraran da su ke da shakku akansu a cikin gari.To sai dai tuni wasu kungiyoyi su ka soma nuna damuwarsu da matakin da su ka ce jami'an tsaron na wuce gona da iri wajen aiwatar da matakan tsaro.A cikin wata sanarwa da ta fitar kawancen kungiyoyin fararan hula na "CADRE" ta bakin shugabansa Abdulmumuni Usmane, ya nuna damuwarsa dangane da
yanda lamarin binciken ke wakana a cikin jahar Agadez.
Ko a birnin Yamai ma dai duk kanwar ja ce, gwamnatin ta karfafa
matakan tsaro a bakin wasu manyan ofisoshinta da na jakadancin
kasashen waje.Majalissar dokokin kasar Nijar na daga cikin
irin wadannan gurare, inda yanzu haka aka haramta shigar duk wani abun hawa na duk wasu mutanan da ba ma'aikatan gurin ba ne ko ma kuma 'yan Majalisa.
Ganin irin yanda wadannan korafe-korafe ne ma su ka soma yin yawa ya sanya Ministan cikin gida Malam Abdu Labo ya kira wani babban taron gangami a birnin Yamai, inda ya bayyanawa al'umma dalilansu na daukar wadannan matakai, da kuma neman goyan bayan al'ummar ga wanann shiri.
Yanzu haka dai gwamnatin ta bada sanarwar gudanar da irin wadannan taruruka na fadakarwa a duk jahahohin kasar da zummar samun goyan bayan al'umma ga wadannan matakai da yace na sabke gyran kayanka ne da ba zai taba zama aje mu raba ba.

Gebäude des Parlaments der Republik Niger, Niamey. Foto: Mahaman Kanta/DW, 19.5.2011, Niamey / Niger, Zulieferer: Thomas Mösch
An karfafa matakan tsaro gaban Majalisar Dokokin NijarHoto: DW
This video grab taken from Niger's TV public channel Tele Sahel on May 23, 2013 shows people standing in front of wreckage of the suicide bomber's motor vehicle, at the Agadez army base, northern Niger, following car bombings in Niger in which at least 20 people died. Islamists groups have claimed responsibility for twin suicide car bombings on an army base and a French-run uranium mine in Niger, in retaliation for the country's military involvement in neighbouring Mali. AFP PHOTO/TELE SAHEL (Photo credit should read STR/AFP/Getty Images)
Harin AgadezHoto: STR/AFP/Getty Images

Mawallafi: Gazali Abdou Tasawa
Edita: Yahouza Sadissou Madobi