Hukumar kiwan lahi ta Majalisar Dinkin Dunia ta kalubalanci masu sarrafa magani a bayan fage
February 16, 2006A wani zaman taro da ke gudanarwa a birnin Rome na kasar Italia,Hukumar kiwon lahia ta Majalisar Dunia Dunia, ta bukaci a kara matsa kaimi, wajen yaki da masu sarrapa maganin assibti na bayan fage.
WHO, kokuma OMS, ta dangata wannan aiki, da kashin kai, ta la`akari da yadda, masu sarrafa maganin ba su da wata cikkakar kurewa, ta fannin kiwon lahia.
Jami´in hukumar lahia ta dunia, mai kulla ta kimiyar kirkiro magani, Howard Zucker, ya bayyana cewar, hukumar, za ta nemi tallafin jami´an tsaron kasa da kasa, wato Interpol, domin taimakawa wajen wannan yaki.
Wani mai magana da yawun kungiyoyin masu saida magani a Pharmacie, kokuma Kyamus, ya shawarwarci tanadar dokoki masu tsanani, ga dukan wanda aka samu, su na sarrafa magani ko su na saida shi a bayan fage.
Ya bada misali da wasu yara a kasar Haiti, da su ka rasa rayuka a sanadiyar shan wani maganin tari, da ya hito daga kasar China, wanda kuma su ka saya, wajen yan saida magani na kan titina.
Kazalika a kasar Kenya, wasu karin mutanen, sun kwanta dama, a dalili da anfani da magani na bayan fage.