1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumar IAEA ta fara cire kyamarorinta a tashoshin nukiliyar Iran

February 12, 2006
https://p.dw.com/p/Bv8T
Kamfanin dillancin labarun Associated Press ya rawaito cewar hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta cire da yawa daga cikin kyamarorin da ta kakkafa a tashoshin nukiliyar Iran, bisa kiran da gwamnatin Teheran ta yi na a yi haka. Kamfanin dillancin labarun ya rawaito majiyoyin ´yan diplomasiya a hedkwatar hukumar IAEA dake birnin Vienna na cewa yanzu hanya guda daya ta ragewa hukumar na gudanar da bincike a tashoshin nukiliyar na Iran. Iran ta bukaci a cire makullayya da kuma kyamarorin bayan da hukumar IAEA ta yanke shawarar yin karar Iran din a gaban kwamitin sulhu na MDD. A jawabin da yayi wa taron gangamin tunawa da juyin juya halin Islama na 1979 a birnin Teheran, a jiya asabar shugaba Mahmud Ahmedi Nijad ya yi barazanar janyewa daga yarjejeniyar da ta hana yaduwar makaman nukiliya a duniya.