1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumar abinci ta majalisar dinkin duniya za ta ƙara kai agaji ga ƙasashen sahel

April 21, 2010

Hukumar cimakka ta majalisar dinkin duniya za ta ƙara ƙarfafa taimako ga ƙasashen Nijar da Cadi dake fama da fari

https://p.dw.com/p/N2UR
taimakon Kayen abinci na hukumar cimakka ta duniya a garin Maradi wani yankin dake a gabacin ƙasar NijarHoto: AP

  Hukumar cimakka ta majalisar dinkin duniya FAO ta bada sanarwa  ƙara ƙarfafa agajin da ta ke bayarwa manoma da makiyaya a ƙasashen Nijar da Cadi wanɗanda ke fuskantar ƙarancin abinci a sakamakon fari da ake fama da shi a ƙasashen sahel.Hukumar ta yi gargaɗin cewa rashin kyaukyawar daminar da ba a samu ba a shekara  bara ba na iya yin barazana ga kimanin mutun miliyion 9,8 a cikin ƙasashen wanda wasu ke cikin halin yunwa a arewacin Burkina Faso da arewa maso gabacin Mali, dakuma Nijar.Ƙungiyar ta FAO ta ce ta ƙaddamar da tsare tsare domin kawo talafi ga al uma a cikin ƙasahen,misali a ƙasar Nijar ta ƙaddamar da projet na dala Amurka miliyion 12 da al uma miliyion biyu da rabi zasu ci moriyarsa.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane

Edita        :  Abdullahi    Tanko   Bala