1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hisbollah ta yi watsi da shawarar dakatar da yaki

July 21, 2006
https://p.dw.com/p/Bupm

Kungiyar Hisbollah ta bi sahun Isra´ila wajen yin watsi da kiran da babban sakataren MDD Kofi Annan ya yi na a tsagaita bude wutar yakin da ake yi tsakanin Isra´ila da Hisbollah. Wakilin Hisbollah a majaliasar dokokin Libanon Hussein Hajj Hasan ya fadawa kamfanin dillancin labarun AFP a yau juma´a cewa abin da zasu amince da shi shi ne wani shirin tsagaita wuta ba tare da gindaya sharadi ba da tattauna batun yin musayar firsinoni. Shi ma shugaban Hisbollah a Libanon Sheikh Hassan Nasrallah ya yi watsi da sakin sojojin Isra´ila da ake garkuwa da su ba tare da an yi musayar su da firsinonin Falasdinawa dake gidajen kurkukun Isra´ila ba. A jiya dai ne Mista Annan ya ba da shawarar a sako sojojin Isra´ila biyu da Hisbolah ta yi garkuwa da su kana kuma a dakatar da yakin nan take.